Skip to main content

Posts

Showing posts with the label Labaran Yammacin Litinin 03/02/2020CE - 08/06/1441AH. Cikakkun labaran

Labaran Yammacin Litinin 03/02/2020CE - 08/06/1441AH. Cikakkun labaran

Labaran Yammacin Litinin 03/02/2020CE - 08/06/1441AH. Cikakkun labaran  Boko Haram sun kashe sojoji 3 sun kwace motocin yaki 2 a Borno.  Gobara ta kama ofishin hukumar INEC a jihar Imo.  Gwamnatin jihar Lagos ta sa an kama mashuna da Keken NAPEP fiye da 250 sakamakon sanya dokar hana achaba a jihar.  Kotu ta yanke wa wasu 'yan fashi da makami biyu hukuncin kisa ta hanyar rataya a Jos.  Sanata Ali Ndume ya koka kan yadda al’amarin tsaro a arewa maso gabas ke kara tabarbarewa, ya yi kira ga  Buhari da ta dauki mataki.  Tsohon gwamnan jihar Zamfara Abdulaziz Yari ya ce lallai idan gwamnatin jihar ta cigaba da kwace filayen jama'a za su yi zanga-zanga.  Ministan Sufuri, Amaechi ya ce gwamnati ba za ta kara farashin tikitin jirgin kasa ba na Kaduna zuwa Abuja domin a bai wa talakawa dama.  Za a bai wa fararen hula makamai domin yaki da ta'addanci a Burkina Faso.  Kungiyar OIC ta yi watsi da shirin shugaba Trump na Amurka na zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.