Skip to main content

Posts

Showing posts with the label TIRKASHI- WATA SABUWA INJI 'YAN CACA

TIRKASHI- WATA SABUWA INJI 'YAN CHA-CHA

Za a kasa kudaden marigayi Abacha tsakanin kasashe uku Najeriya da Amurka da tsibirin Jersey sun ce za su kasafta fiye da dala milyan 267 da tsibirin Jersey ya kwace daga irin kudaden da ake zargin gwamnatin tsohon shugaban Najeriya na soja, marigayi janar Sani Abacha ta sata ta jibge a bankunan kasar. A ranar Juma'ar da ta gabata ne dai aka sanya dala 267 a cikin wani asusu na musamman da gwamnatin kasar ta Jersey ta kafa domin zuba irin wadannan kudade masu kama da ganima. Wani wakili daga ofishin ministan shari'ar kasar ya shaida wa BBC cewa har kawo yanzu Jersey ba ta kammala tantance hanyar da za ta bi ba wajen kasafta kudaden ba. Sai dai ya ce gwamnatin tsibirin za ta zauna da Najeriya da Amurka domin tattauna yadda za su raba kudin a tsakaninsu. Gwamnatin Najeriya za ta rabawa talakawa kudaden Abacha 'Kudin da Abacha ya sace': Switzerland za ta mayar wa Nigeria $320m A baya dai wata kotu a Amurka ta gano kudaden wadanda ta ce an fitar da su daga Najeriya ta wasu

Abdul-salam baba ahmad

Allah ya yiwa tsohon kwamishinan Kaduna, Abdulsalam Baba Ahmed rasuwa Updated: 10 hours ago Author: ibrahim sani hussain Views: 2335 Category: Labarai FACEBOOK EMAIL TWITTER WHATSAPP FACEBOOK MESSENGER TELEGRAM - Tsohon kwamishinan filaye na jihar Kaduna, Abdulsalam Baba Ahmed ya rasu, a ranar Talata, 4 ga watan Yuni bayan yayi fama da rashin lafiya - Babban dan Marigayin, Hakeem Baba Ahmed ne ya tabbatar da rasuwar mahaifin nasa ga manema labarai - Anyi jana'izarsa a gidan ahlin Baba Ahmed da ke Tudun Wada, Zaria a yau Talata Allah ya yiwa tsohon kwamishinan filaye na jihar Kaduna, Abdulsalam Baba Ahmed rasuwa, a ranar Talata, 4 ga watan Yuni bayan yayi fama da rashin lafiya. Marigayin ya rasu yana da shekaru 53 a duniya. Babban dansa, Hakeem Baba Ahmed ne ya sanar da hakan ga manema labarai a garin Zaria. Ya bayyana cewa mahaifin nasa ya rasu da misalin karfe 3:00 na rana a Kaduna. Kafin a nada shi a matsayin kwamishina a gwamnatin Ramalan Yero, marigayin yayi aiki a matsayin shu