Skip to main content

Posts

Showing posts with the label KUDIRIN ADDINI
MENENE MA A CIKI TUKUN?. Zan danyi magana ne akan wani abu danaga yana yawan faruwa da yan uwa mata da maza, sau da yawa inna fahimci hakan ko naga wani yana magana da korafi, sai tunani ya fara ciyartar zuciyata. Menene ke haifar da akasarin lalacewar soyayya tsakanin mata da maza? Sai karamin tunani irin ta kwakwalwata yakaini ga wata matsaya, matsayar kuwa itace; Son Shahara. Ko wacce Mace yanzu burinta shine tazama ta sami saurayi ko ince mijin da zata aura yazama shahararre, Shara a kudi, ilimi, ko Wani Babban aiki ko uwa ubama abin da suka fi so shine ace mutum yana karatu a Kasar waje. Wannan yayi tasiri gaya a zukatan mutane, basu duba zuciyar mutum da kuma hadafinsa kan tafiyar addini, sau tari abinda kake tunanin mutum, sai kaga daga baya ka fahimci ba haka yake ba, me yasa?. Saboda ka biyo wani abu ne da kake ganin yana dashi, dazarar ka fahimci hakikaninsa saikai tunanin canza reshen da kake kai, wannan yasa soyayyar yan uwanmu mata da maza bata kai labari mafi

DUNIYA MAKARANTA

*DUNIYA MAKARANTA * "Ma'aunin gane mai arziki shine a duba ni'imar da yake da ita wanda kudi basu samar da ita." *Dr. Mansur Sokoto .* * DUNIYA MAKARANTA * "Idan rayuwar ka tana cikin jin dadi, zaka rika ganin komai kyakykyawa ne a idonka. Idan kana da koshin zuci kadan zai wadace ka. Idan ka yarda da Allah komai sai yazo maka cikin sauki." *Dr. Mansur Sokoto.* * DUNIYA MAKARANTA * "Abu biyu ne suke daga darajar dan Adam: Amfanin jama'a da hakurin cutarwar su. Abu biyu kuwa suna tunkude musiba: sadaka da sada zumunci." *Dr. Mansur Sokoto.* *DUNIYA MAKARANTA * "Idan ka fadawa mutum gaskiya, kamar ka shayar dashi kofin madaci ne. Bai kamata kayi tsammanin ya gode maka ba." * Dr. Mansur Sokoto.* *DUNIYA MAKARANTA * "Duniya abun hawar ka ce, idan ka tuka ta sai ta kaika inda kake so. Amma idan ta tuka ka to zata kai ka mahallaka." *Dr. Mansur Sokoto* *DUNIYA MAKARANTA* "Duk yadda ibada tayi tsanani wah