Skip to main content
MENENE MA A CIKI TUKUN?.

Zan danyi magana ne akan wani abu danaga yana yawan faruwa da yan uwa mata da maza, sau da yawa inna fahimci hakan ko naga wani yana magana da korafi, sai tunani ya fara ciyartar zuciyata.

Menene ke haifar da akasarin lalacewar soyayya tsakanin mata da maza? Sai karamin tunani irin ta kwakwalwata yakaini ga wata matsaya, matsayar kuwa itace; Son Shahara.

Ko wacce Mace yanzu burinta shine tazama ta sami saurayi ko ince mijin da zata aura yazama shahararre, Shara a kudi, ilimi, ko Wani Babban aiki ko uwa ubama abin da suka fi so shine ace mutum yana karatu a Kasar waje.

Wannan yayi tasiri gaya a zukatan mutane, basu duba zuciyar mutum da kuma hadafinsa kan tafiyar addini, sau tari abinda kake tunanin mutum, sai kaga daga baya ka fahimci ba haka yake ba, me yasa?.

Saboda ka biyo wani abu ne da kake ganin yana dashi, dazarar ka fahimci hakikaninsa saikai tunanin canza reshen da kake kai, wannan yasa soyayyar yan uwanmu mata da maza bata kai labari mafi yawan lokuta.

Wani zakaga yana da budurwa amma yana sonta ne don yaga kamar tana da wani abu dazarar ya zauna ya karanceta sarai saisu zama sun "BreakUp" me yasa?.

Dama wannan abinda take dashi ya biyo, kuma ya gane babu shi, hakama mata, yakamata mu zauna muyi wa kanmu karatun ta natsu, mu so juna don Allah, mu gina soyayyar kan tafarkin Allah tare da neman zabin alkhairi dake ciki.

Wannan shiya fi dacewa damu, ba neman shahara ko suna a cikin kawaye ko abokai ba, kai burinka a ce kaine saurayin wance mai kaza da kaza ko yar gidan wane.

Ke kuma kawaye suyita famfa ki kina sahan kamshi ala dole kina soyayya da mai karatu a kasar waje ko wani sanannen mutum ko mai kudi.

Mecece ribar da za'a girba a wannan ginin tubalin tokar da zai iya gushewa wata rana? Addini baibar komi ba saida ya warware  mana shi, ka nema sanin yadda ake fara neman masoyi da yadda zaka sami masoyi na gari mai riko da addini.

Domin da yawan lokuta wajen da kake tunanin samun farin ciki da walwalar da zata baka damar yin ibada cikin tsafta, sai kaga baka samu ba, ya kamata mu hankalta.

Ina rokon Allah mai girma da buwaya Ni da Ku ya datar da mu ga hanya mafi dacewa tafarkin tsira da amincewar Allahu swt domin babu abinda ke bayansu sai dacewa da gidan Al-jannatul firdous.

(Khayri the daughter of islaam).

Comments

elbasawee.com said…
Allah yasaka da alkhairi

Popular posts from this blog

A MAN WAS CRYING

A man was crying😭 and someone asked him why he was crying. And he said I have only one son, I have done all my possible best to educate him so that he will be a great person and by Allah's grace he has been able to acquire all certificates including: 🌺 J.S.C.E. 🌺 S.S.C.E. 🌺 Bachelor's Degree. 🌺 MSc. 🌺 Phd. BUT! Unfortunately, he fell sick and doctors said they can't do anything about his condition and the only option is to die in the next 30 minutes and my son told me to bring all his certificates and I brought them. All he could say was; father, these are my degrees but you never told me to study my Qur'an. I don't know what I'm going to tell Allah! Most of us will not share this message because it is not an interesting joke. But if you are willing enough to share this message, please do so and Allah will never forget what you have done. PLEASE LET US TAKE NOTE OF THESE: 🌹Study the Qur'an like the way you study your notes when it is exams

Labarin 'yan shi'a

Labari da dumi duminsa    'Yan Shi'a sun dakatar da zanga-zanga, sun bayyana dalilansu Kungiyar Islamic Movement in Nigeria (IMN) ta aka fi sani da Shi'a ta sanar da cewa za ta dakatar da zanga-zangar da ta keyi na dan wani lokaci. Shugaban fanin yada labarai na kungiyar ta IMN, Ibrahim Musa ne ya sanar da hakan cikin wata jawabi da ya fitar a ranar Laraba. Gwamnatin Tarayya ta ayyana kungiyar a matsayin na ta'addanci tare da haramta ayyukan kungiyar bayan kotun tarayya da ke Abuja ya ayyana kungiyar a matsayin na ta'addanci. Musa ya ce an dauki matakin dakatar da zanga-zangar ne sakamakon 'wasu sabbin hanyoyi da suke bude na warware matsalar' da ke da alaka da haramta ayyukan kungiyar. Ya ce kungiyar ta dauki matakin dakatar da zanga-zangar ne saboda girmama wasu manyan mutane da suka saka baki kan batun . Ya kara da cewa idan har aka samu wasu suna zanga-zanga a wani sashi na kasar, hakan ka iya faruwa ne idan wasu ba su fahimci sakonsa ba ko kuma sharri

TIRKASHI- WATA SABUWA INJI 'YAN CHA-CHA

Za a kasa kudaden marigayi Abacha tsakanin kasashe uku Najeriya da Amurka da tsibirin Jersey sun ce za su kasafta fiye da dala milyan 267 da tsibirin Jersey ya kwace daga irin kudaden da ake zargin gwamnatin tsohon shugaban Najeriya na soja, marigayi janar Sani Abacha ta sata ta jibge a bankunan kasar. A ranar Juma'ar da ta gabata ne dai aka sanya dala 267 a cikin wani asusu na musamman da gwamnatin kasar ta Jersey ta kafa domin zuba irin wadannan kudade masu kama da ganima. Wani wakili daga ofishin ministan shari'ar kasar ya shaida wa BBC cewa har kawo yanzu Jersey ba ta kammala tantance hanyar da za ta bi ba wajen kasafta kudaden ba. Sai dai ya ce gwamnatin tsibirin za ta zauna da Najeriya da Amurka domin tattauna yadda za su raba kudin a tsakaninsu. Gwamnatin Najeriya za ta rabawa talakawa kudaden Abacha 'Kudin da Abacha ya sace': Switzerland za ta mayar wa Nigeria $320m A baya dai wata kotu a Amurka ta gano kudaden wadanda ta ce an fitar da su daga Najeriya ta wasu