Allah ya yiwa tsohon kwamishinan Kaduna, Abdulsalam Baba Ahmed rasuwa
Updated: 10 hours ago
Author: ibrahim sani hussain
Views: 2335
Category: Labarai
FACEBOOK EMAIL
TWITTER WHATSAPP
FACEBOOK MESSENGER TELEGRAM
- Tsohon kwamishinan filaye na jihar Kaduna, Abdulsalam Baba Ahmed ya rasu, a ranar Talata, 4 ga watan Yuni bayan yayi fama da rashin lafiya
- Babban dan Marigayin, Hakeem Baba Ahmed ne ya tabbatar da rasuwar mahaifin nasa ga manema labarai
- Anyi jana'izarsa a gidan ahlin Baba Ahmed da ke Tudun Wada, Zaria a yau Talata
Allah ya yiwa tsohon kwamishinan filaye na jihar Kaduna, Abdulsalam Baba Ahmed rasuwa, a ranar Talata, 4 ga watan Yuni bayan yayi fama da rashin lafiya.
Marigayin ya rasu yana da shekaru 53 a duniya.
Babban dansa, Hakeem Baba Ahmed ne ya sanar da hakan ga manema labarai a garin Zaria. Ya bayyana cewa mahaifin nasa ya rasu da misalin karfe 3:00 na rana a Kaduna.
Kafin a nada shi a matsayin kwamishina a gwamnatin Ramalan Yero, marigayin yayi aiki a matsayin shugaban karamar hukumar Zaria, sannan ya riki mukamai daban-daban a gwamnati na kungiyoyi masu zaman kansu.
Anyi sallar jana’izarsa a gidan ahlin Baba Ahmed da ke Tudun Wada, Zaria
Kungiyar IZALA tayi Allah wadai da cin Mutunci da yan kwankwasiyya suka yiwa Dr. Ali Pantami Daga Ibrahim Baba Suleiman Kungiyar wa'azin musulunci ta Izalatil Bid'ah wa Iqamatis Sunnah a Naijeriya, Tayi Allah wadai da cin Mutuncin da 'yan kungiyar kwankwasiyya sukayi wa ministan sadarwan Naijeriya Sheikh Dr. Isa Ali Pantami a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano dake Birnin kano. Shugaban IZALA Sheikh (Dr) Abdullahi Bala Lau, shi yayi wannan kira ta wayar tarho daga Birnin Maiduguri jihar Borno a tarayyar Naijeriya, inda yake halartar wani taro a Birnin na Shehu. Sheikh Bala Lau yace, wannan al'amari akwai damuwa kwarai cikinsa, Malami mahaddacin Al'qur'ani, masanin tafsiri, Wanda ya kare rayuwarsa wajen aiki da fadakarwa akan addinin Musulunci, shine wasu 'yan Siyasa zasu masa irin wannan cin Mutunci tabbas an aikata laifi Babba. Shehin Malamin yayi kira da babbar murya cewa jagoran kwankwasiyya Dr. Rabi'u Musa kwankwaso ya fito ya baiwa ya...
Comments