Skip to main content
Kudirin addini: CAN da JNI sun sha ban-ban a Jihar Kaduna Updated: 7 hours ago Author: Muhammad Malumfashi Views: 2300 Category: Labarai , Siyasa FACEBOOK EMAIL TWITTER WHATSAPP FACEBOOK MESSENGER TELEGRAM Kungiyoyin addini a jihar Kaduna sun nuna mabanbantan ra’ayi a game da sabuwar dokar addinin da za a kawo. A Ranar Juma’a 7 ga Watan Yuni, 2019, ne majalisar dokokin jihar ta amince da wannan kudiri. Mista Sunny Akanni, wanda ya na cikin manyan kungiyar Pentecostal Fellowship of Nigeria (PFN), yayi barazanar maka majalisar dokokin jihar Kaduna a kotu, a dalilin amincewa da wannan kudiri da ya kawo surutu. Akanni yake cewa majalisar jihar Kaduna ta sabawa umarnin kotu na rattaba hannu a kan wannan doka da zai yi wa sha’anin addini garambawul. PFN tace maganar ta na gaban kotu amma majalisa ta yi mursisi. Haka zalika kungiyar CAN ta bayyana cewa za ta duba wannan kudiri, inda ta nuna cewa ta na da ja da wannan doka da ake shirin kawowa. Shugaban kiristocin jihar Kaduna, Joseph Hayab ya bayyana wannan. KU KARANTA: Lashe zabe dabam da sa-hannun Sanatoci a Majalisa – Ndume Ita kuma kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI), ta yi farin ciki da jin labarin wannan doka. Yusuf Adamu, wanda shi ne Sakataren kungiyar JNI ya fito ya ce babu wata matsala tattare da wannan kudiri da aka kawo. Yusuf Adamu yake cewa duk wanda zai yi wa’azi yadda ya dace bai kamata ya ji tsoron dokar da za a kawo ba. Kungiyar tace CAN ba ta bada gudumuwa yadda aka nema ba a lokacin da ake shirin kawo wannan kudiri. Kungiyar ta Jama’atu Nasril Islam, tace a lokacin da aka nemi bangarorin addini su sa na su bakin wajen kawo wannan sabuwar doka da za ta yi wa addini garambawul, CAN ta zare jikin tane gaba daya. Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

Comments

Popular posts from this blog

A MAN WAS CRYING

A man was crying😭 and someone asked him why he was crying. And he said I have only one son, I have done all my possible best to educate him so that he will be a great person and by Allah's grace he has been able to acquire all certificates including: 🌺 J.S.C.E. 🌺 S.S.C.E. 🌺 Bachelor's Degree. 🌺 MSc. 🌺 Phd. BUT! Unfortunately, he fell sick and doctors said they can't do anything about his condition and the only option is to die in the next 30 minutes and my son told me to bring all his certificates and I brought them. All he could say was; father, these are my degrees but you never told me to study my Qur'an. I don't know what I'm going to tell Allah! Most of us will not share this message because it is not an interesting joke. But if you are willing enough to share this message, please do so and Allah will never forget what you have done. PLEASE LET US TAKE NOTE OF THESE: 🌹Study the Qur'an like the way you study your notes when it is exams

Labarin 'yan shi'a

Labari da dumi duminsa    'Yan Shi'a sun dakatar da zanga-zanga, sun bayyana dalilansu Kungiyar Islamic Movement in Nigeria (IMN) ta aka fi sani da Shi'a ta sanar da cewa za ta dakatar da zanga-zangar da ta keyi na dan wani lokaci. Shugaban fanin yada labarai na kungiyar ta IMN, Ibrahim Musa ne ya sanar da hakan cikin wata jawabi da ya fitar a ranar Laraba. Gwamnatin Tarayya ta ayyana kungiyar a matsayin na ta'addanci tare da haramta ayyukan kungiyar bayan kotun tarayya da ke Abuja ya ayyana kungiyar a matsayin na ta'addanci. Musa ya ce an dauki matakin dakatar da zanga-zangar ne sakamakon 'wasu sabbin hanyoyi da suke bude na warware matsalar' da ke da alaka da haramta ayyukan kungiyar. Ya ce kungiyar ta dauki matakin dakatar da zanga-zangar ne saboda girmama wasu manyan mutane da suka saka baki kan batun . Ya kara da cewa idan har aka samu wasu suna zanga-zanga a wani sashi na kasar, hakan ka iya faruwa ne idan wasu ba su fahimci sakonsa ba ko kuma sharri

TIRKASHI- WATA SABUWA INJI 'YAN CHA-CHA

Za a kasa kudaden marigayi Abacha tsakanin kasashe uku Najeriya da Amurka da tsibirin Jersey sun ce za su kasafta fiye da dala milyan 267 da tsibirin Jersey ya kwace daga irin kudaden da ake zargin gwamnatin tsohon shugaban Najeriya na soja, marigayi janar Sani Abacha ta sata ta jibge a bankunan kasar. A ranar Juma'ar da ta gabata ne dai aka sanya dala 267 a cikin wani asusu na musamman da gwamnatin kasar ta Jersey ta kafa domin zuba irin wadannan kudade masu kama da ganima. Wani wakili daga ofishin ministan shari'ar kasar ya shaida wa BBC cewa har kawo yanzu Jersey ba ta kammala tantance hanyar da za ta bi ba wajen kasafta kudaden ba. Sai dai ya ce gwamnatin tsibirin za ta zauna da Najeriya da Amurka domin tattauna yadda za su raba kudin a tsakaninsu. Gwamnatin Najeriya za ta rabawa talakawa kudaden Abacha 'Kudin da Abacha ya sace': Switzerland za ta mayar wa Nigeria $320m A baya dai wata kotu a Amurka ta gano kudaden wadanda ta ce an fitar da su daga Najeriya ta wasu