Skip to main content

YANZU YANZU BOKO KARAM SUN AMSHE WANI GARI AMAIDUGURI

Yanzu Yanzu: Boko Haram sun karbe wani gari a Borno
Updated: 2 hours ago
Author: Abubakar Nura Bala
Views: 1350
Category: Labarai
FACEBOOK EMAIL
TWITTER WHATSAPP
FACEBOOK MESSENGER TELEGRAM
Rahotanni da ke zuwa mana daga jaridar Daily Trust ya nuna cewa a ranar Lahadi, 2 ga watan Yuni yan Boko Haram sun amshe garin Marte, hedkwatar karamar hukumar Marte dake jihar Borno.
Daya daga cikin majiyan da suka tabbatar da lamarin, yace yan ta’addan sun shigo sansanin rundunar sojin bataliya na 133, inda suke ta harbe-harbe ba kakkautawa sannan a sanadiyar haka suka kacalcala komai.
“Da alama yan ta’addan basu zo da niyyar illata yan farar hula ba, sun zo ne da niyyan amshe garin, wannan yasa suka shiga sansanin sojojin ba tare da sanarwa ba da misalin karfe 6pm, kimanin kasa da awa daya kafin lokacin bude baki,” majiyar ta tabbatar.
Wani majiyi ya kuma bayyana cewa sun yi arangama da yan ta’addan inda saur kiris su yi gababa a kansu.
Ya kara da cewa “Ina iya fada muku cewa muna dab da cin galaba akansu; amman Allah ne masanin dabaru da suka yi amfani da shi, wanda hakan yasa suka yi nasara a kanmu; a halin yanzu garin ya koma karkashin kulawansu.”
A cewar wani majiyin da ya tsere, “baza a iya tabbatar da adadin wadanda suka ji rauni ba a bangaren biyu bayan duk mun tsere cikin daji guda, inda yawancinmu suka nemi hanya zuwa Maiduguri sannan har yanzu yawanci suna cikin jeji suna neman mafita."

Comments

Popular posts from this blog

A MAN WAS CRYING

A man was crying😭 and someone asked him why he was crying. And he said I have only one son, I have done all my possible best to educate him so that he will be a great person and by Allah's grace he has been able to acquire all certificates including: 🌺 J.S.C.E. 🌺 S.S.C.E. 🌺 Bachelor's Degree. 🌺 MSc. 🌺 Phd. BUT! Unfortunately, he fell sick and doctors said they can't do anything about his condition and the only option is to die in the next 30 minutes and my son told me to bring all his certificates and I brought them. All he could say was; father, these are my degrees but you never told me to study my Qur'an. I don't know what I'm going to tell Allah! Most of us will not share this message because it is not an interesting joke. But if you are willing enough to share this message, please do so and Allah will never forget what you have done. PLEASE LET US TAKE NOTE OF THESE: 🌹Study the Qur'an like the way you study your notes when it is exams

Labarin 'yan shi'a

Labari da dumi duminsa    'Yan Shi'a sun dakatar da zanga-zanga, sun bayyana dalilansu Kungiyar Islamic Movement in Nigeria (IMN) ta aka fi sani da Shi'a ta sanar da cewa za ta dakatar da zanga-zangar da ta keyi na dan wani lokaci. Shugaban fanin yada labarai na kungiyar ta IMN, Ibrahim Musa ne ya sanar da hakan cikin wata jawabi da ya fitar a ranar Laraba. Gwamnatin Tarayya ta ayyana kungiyar a matsayin na ta'addanci tare da haramta ayyukan kungiyar bayan kotun tarayya da ke Abuja ya ayyana kungiyar a matsayin na ta'addanci. Musa ya ce an dauki matakin dakatar da zanga-zangar ne sakamakon 'wasu sabbin hanyoyi da suke bude na warware matsalar' da ke da alaka da haramta ayyukan kungiyar. Ya ce kungiyar ta dauki matakin dakatar da zanga-zangar ne saboda girmama wasu manyan mutane da suka saka baki kan batun . Ya kara da cewa idan har aka samu wasu suna zanga-zanga a wani sashi na kasar, hakan ka iya faruwa ne idan wasu ba su fahimci sakonsa ba ko kuma sharri

TIRKASHI- WATA SABUWA INJI 'YAN CHA-CHA

Za a kasa kudaden marigayi Abacha tsakanin kasashe uku Najeriya da Amurka da tsibirin Jersey sun ce za su kasafta fiye da dala milyan 267 da tsibirin Jersey ya kwace daga irin kudaden da ake zargin gwamnatin tsohon shugaban Najeriya na soja, marigayi janar Sani Abacha ta sata ta jibge a bankunan kasar. A ranar Juma'ar da ta gabata ne dai aka sanya dala 267 a cikin wani asusu na musamman da gwamnatin kasar ta Jersey ta kafa domin zuba irin wadannan kudade masu kama da ganima. Wani wakili daga ofishin ministan shari'ar kasar ya shaida wa BBC cewa har kawo yanzu Jersey ba ta kammala tantance hanyar da za ta bi ba wajen kasafta kudaden ba. Sai dai ya ce gwamnatin tsibirin za ta zauna da Najeriya da Amurka domin tattauna yadda za su raba kudin a tsakaninsu. Gwamnatin Najeriya za ta rabawa talakawa kudaden Abacha 'Kudin da Abacha ya sace': Switzerland za ta mayar wa Nigeria $320m A baya dai wata kotu a Amurka ta gano kudaden wadanda ta ce an fitar da su daga Najeriya ta wasu