Skip to main content

SHUGABA BUHARI ZAI TAFI LIBERIA

Shugaba Buhari zai daga zuwa kasar Liberia don halartar taro da kuma karbar wata muhimmiyar kyauta a kasar
 Written by Ibrahim sani hussain 17 minutes ago - Shugaban kasa Buhari zai daga zuwa kasar Liberia a ranar Juma'a, 25 ga watan Yuli - Buhari zai halarci taron taron bikin samun 'yancin kan kasar sannan zai karbi lambar yabo na musamman a kasar - Daga cikin wadanda za su masa rakiya akwai gwamnoni uku, sakataren dindindin na ma'aikatar harkokin waje da wasu manyan jami'an gwamnati Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bar Abuja a ranar Juma’a, 25 ga watan Yuli zuwa Monrovia, kasar Liberia domin halartan bikin zagayowar raanar yancin kan kasar karo na 172. Bayan kasancewarsa babban bako na musamman a wajen taron, za a karrama Shugaban kasar da karramawa mafi daraja a kasar. A wani jawabi daga babban hadimin Shugaban kasar a kafofin watsa labarai, Garba Shehu, ya kuma bayyana cewa gwamnatin kasar ce za ta gabatar da lambar yabon ga Buhari akan kokarinsa kan lamuran kasashen duniya, gwamnati, addini, da dai sauransu. Shugaban kasar zai samu rakiyar wasu gwamnoni da suka hada da Kayode ayemi, Abdulrahman Abdulrazaq da kuma Mai Mala Buni. Sauran masu rakiyan sun hada da sakataren dindindi na ma’aikatar harkokin waje, Ambasada Mustapha Sulaiman da sauaran manyan jami’an gwamnati.

Comments

Popular posts from this blog

Kungiyar IZALA tayi Allah wadai da cin Mutunci da yan kwankwasiyya suka yiwa Dr. Ali Pantami

Kungiyar IZALA tayi Allah wadai da cin Mutunci da yan kwankwasiyya suka yiwa Dr. Ali Pantami Daga Ibrahim Baba Suleiman Kungiyar wa'azin musulunci ta Izalatil Bid'ah wa Iqamatis Sunnah a Naijeriya, Tayi Allah wadai da cin Mutuncin da 'yan kungiyar kwankwasiyya sukayi wa ministan sadarwan Naijeriya Sheikh Dr. Isa Ali Pantami a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano dake Birnin kano. Shugaban IZALA Sheikh (Dr) Abdullahi Bala Lau, shi yayi wannan kira ta wayar tarho daga Birnin Maiduguri jihar Borno a tarayyar Naijeriya, inda yake halartar wani taro a Birnin na Shehu. Sheikh Bala Lau yace, wannan al'amari akwai damuwa kwarai cikinsa, Malami mahaddacin Al'qur'ani, masanin tafsiri, Wanda ya kare rayuwarsa wajen aiki da fadakarwa akan addinin Musulunci, shine wasu 'yan Siyasa zasu masa irin wannan cin Mutunci tabbas an aikata laifi Babba. Shehin Malamin yayi kira da babbar murya cewa jagoran kwankwasiyya Dr. Rabi'u Musa kwankwaso ya fito ya baiwa ya...
DAKIN LABAREN  HAUSA 23 sep 2019 AURE KO ZAMAN GIDA? 1 - 2 AURE KO ZAMAN GIDA?    AURE KO ZAMAN GIDA? •••••••PART  1 ••••••••  HAUWA M.JABO akan hanyar asibiti nida qawata zeenah khalifa zamuje duba wata maqociyarmu da batada lafiya,Muna shiga asibiti mukayi karo da wata mata da yara guda biyu a hannunta zenah khalifa tayi sokoko tana kallonta.Ke zeenah khalifa kinji haushi ki kalli maza ki kalli mata.! Banason wulaqanci hauwa jabo.! Mikike nufi da inkalli mata in kalli maza? kamar wata bunsura..!!! Na kwashe dadariya nace yanzu dai yimin bayani mi kika hango.?? Ta kwashe da dariya kibari kawai,Hauwa jabo matar nan ta hadu billahillazi..Da ace ba baqa bace sai ince wllhy ba indiyace keni muje muyi qawance da ita,Ke zainab muna fama da talaucinmu za...