Skip to main content
Shugaban Tunisia Beji Caid Essebsi ya rasu Fadar shugaban kasar Tunisia ta sanar da mutuwar shugabanta Beji Caid Essebsi, wanda ya mutu yana da shekara 92. Shi ne shugaban kasar da ya fi kowa tsufa a duniya. An kwantar da shi a asibiti ranar Laraba amma jami'ai ba fadi dalilin rashin lafiyar tasa ba. A shekerar 2014 ne Mista Essebsi ya lashe zaben farko na kasa tun bayan boren kasashen Larabawa. Mista Essebsi ya kuma kwanta a asibiti a watan da ya gabata bayan fama da abin da jami'ai suka kira "rashin lafiya mai tsanani." Ba su yi karin bayani kan batun ba. Firai Minista Youssef Chahed, wanda ya ziyarce shi a asibiti, ya roki mutane da su daina yada "labaran karya" a kan halin da shugaban ke ciki. A tsarin kundin tsarin mulkin kasar, Mista Chahed zai iya zama shugaban kasa na tsawon kwanakin da ba za su wuce 60 ba ko kuma zuwa lokacin da za a zabi sabon shugaba. A farkon shekarar nan ne ya sanar da cewa ba zai tsaya a zaben da za a sake yi a watan Nuwamba ba. A wani taro ya shaida wa jam'iyyarsa ta Nidaa Tounes cewa ya kamata wani mai jini a jika ya karbi ragamar. Ya ce lokaci ya yi da "za a bai wa matasa dama." Mista Essebsi tsohon lauya ne da ya yi karatu a birnin Paris na Faransa. A lokacin da yake dan siyasa na tsawon lokaci ya kuma yi ministan harkokin cikin gida da kuma kakakin majalisar wakilai. A shekarar 2011 ne aka hambarar da tsohon shugaban Tunisiya Zine el-Abedine Ben bayan shafe shekara 23 a kan mulki. Tun sannan ake jinjinawa Tunisiya kasancewarta kasar da ita kadai ta hau turbar dimokradiyya bayan boren kasashen Larabawa. Sai dai a shekarun baya-bayan nan kasar ta sha fama da hare-haren masu ikirarin jihadi da kuma tabarbarewar tattalin arziki, inda yawan marasa aikin yi ke ta'azzara. Labarai masu alaka Tunisiya Tura wannan labarin Game da aika wa Koma sama Kewaye a shafin BBC Copyright © 2019 BBC. BBC ba za ta dauki alhakin abin da ke kunshi a wasu shafukan na daban ba. Karanta tsarinmu game da bakin shafuka. AFP

adamusuleimanbasawa@gmail.com

Comments

Popular posts from this blog

A MAN WAS CRYING

A man was crying😭 and someone asked him why he was crying. And he said I have only one son, I have done all my possible best to educate him so that he will be a great person and by Allah's grace he has been able to acquire all certificates including: 🌺 J.S.C.E. 🌺 S.S.C.E. 🌺 Bachelor's Degree. 🌺 MSc. 🌺 Phd. BUT! Unfortunately, he fell sick and doctors said they can't do anything about his condition and the only option is to die in the next 30 minutes and my son told me to bring all his certificates and I brought them. All he could say was; father, these are my degrees but you never told me to study my Qur'an. I don't know what I'm going to tell Allah! Most of us will not share this message because it is not an interesting joke. But if you are willing enough to share this message, please do so and Allah will never forget what you have done. PLEASE LET US TAKE NOTE OF THESE: 🌹Study the Qur'an like the way you study your notes when it is exams

Labarin 'yan shi'a

Labari da dumi duminsa    'Yan Shi'a sun dakatar da zanga-zanga, sun bayyana dalilansu Kungiyar Islamic Movement in Nigeria (IMN) ta aka fi sani da Shi'a ta sanar da cewa za ta dakatar da zanga-zangar da ta keyi na dan wani lokaci. Shugaban fanin yada labarai na kungiyar ta IMN, Ibrahim Musa ne ya sanar da hakan cikin wata jawabi da ya fitar a ranar Laraba. Gwamnatin Tarayya ta ayyana kungiyar a matsayin na ta'addanci tare da haramta ayyukan kungiyar bayan kotun tarayya da ke Abuja ya ayyana kungiyar a matsayin na ta'addanci. Musa ya ce an dauki matakin dakatar da zanga-zangar ne sakamakon 'wasu sabbin hanyoyi da suke bude na warware matsalar' da ke da alaka da haramta ayyukan kungiyar. Ya ce kungiyar ta dauki matakin dakatar da zanga-zangar ne saboda girmama wasu manyan mutane da suka saka baki kan batun . Ya kara da cewa idan har aka samu wasu suna zanga-zanga a wani sashi na kasar, hakan ka iya faruwa ne idan wasu ba su fahimci sakonsa ba ko kuma sharri

TIRKASHI- WATA SABUWA INJI 'YAN CHA-CHA

Za a kasa kudaden marigayi Abacha tsakanin kasashe uku Najeriya da Amurka da tsibirin Jersey sun ce za su kasafta fiye da dala milyan 267 da tsibirin Jersey ya kwace daga irin kudaden da ake zargin gwamnatin tsohon shugaban Najeriya na soja, marigayi janar Sani Abacha ta sata ta jibge a bankunan kasar. A ranar Juma'ar da ta gabata ne dai aka sanya dala 267 a cikin wani asusu na musamman da gwamnatin kasar ta Jersey ta kafa domin zuba irin wadannan kudade masu kama da ganima. Wani wakili daga ofishin ministan shari'ar kasar ya shaida wa BBC cewa har kawo yanzu Jersey ba ta kammala tantance hanyar da za ta bi ba wajen kasafta kudaden ba. Sai dai ya ce gwamnatin tsibirin za ta zauna da Najeriya da Amurka domin tattauna yadda za su raba kudin a tsakaninsu. Gwamnatin Najeriya za ta rabawa talakawa kudaden Abacha 'Kudin da Abacha ya sace': Switzerland za ta mayar wa Nigeria $320m A baya dai wata kotu a Amurka ta gano kudaden wadanda ta ce an fitar da su daga Najeriya ta wasu